Jami'ar Yusuf Maitama Sule Kano, tsohon sunan ta na da Northwest University Kano Jami'a ce mallakin gwamnatin jahar Kano mai mazaunin wucin gadi a tsakiyar birnin na Kano da kuma mazaunin dindindin a kan titin Gwarzo cikin birnin na Kano.
Tana daga cikin jami'o'in da suka kafu a shekarar 2012 kuma tasamu amincewar hukumar kula da jami'o'i ta ƙasa wato NUC.
Jami'ar Yusuf Maitama Sule | |
---|---|
| |
Bayanai | |
Iri | jami'a |
Ƙasa | Najeriya |
Tarihi | |
Ƙirƙira | 2012 |
yumsuk.edu.ng |
Jami'ar ta Yusuf Maitama Sule University, Kano an ƙirƙireta a shekarar 2012 lokacin gwamnatin Rabiu Musa Kwankwaso domin bunƙasa tsohuwar jahar Arewa maso Yammacin Najeriya kuma aka yi mata laƙani da North-West University wato Jami'ar Arewa maso Yamma. Sai dai daga baya Gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta canza sunan Jami'ar zuwa Yusuf Maitama Sule University domin girmamawa ga Tsohon sanannen ɗan siyasar nan na Najeriya kuma babban dattijon ƙasar wato marigayi Alhaji Yusuf Maitama Sule. An kafa Jami'ar ne domin bunƙasa ilimi ba kawai a yankin na Arewa maso yamma ba harma da ƙasar daba Nahiyar Afrika baki daya.
This article uses material from the Wikipedia Hausa / هَوُسَ article Jami'ar Yusuf Maitama Sule, which is released under the Creative Commons Attribution-ShareAlike 3.0 license ("CC BY-SA 3.0"); additional terms may apply (view authors). An samar da dukkan muƙaloli a ƙarƙashin lasisin Creative Commons Attribution/Share-Alike; tana yiwuwa wasu ƙa'idoji su yi tasiri. Ku duba Ka'idojin Amfani na Gidauniyar Wiki domin ƙarin bayani. Images, videos and audio are available under their respective licenses.
®Wikipedia is a registered trademark of the Wiki Foundation, Inc. Wiki Hausa / هَوُسَ (DUHOCTRUNGQUOC.VN) is an independent company and has no affiliation with Wiki Foundation.