Senata Mohammed Danjuma Goje (an haife shi a ranar 10 ga watan Oktoban 1952), a Pindiga, Akko,Jihar Gombe an,zaɓe shi gwamnan Jihar Gombe a shekara ta 2003 ƙarƙashin jam'iyar PDP, ya kama aiki daga ranar 29 ga watan Mayun 2003, ya sake cin zabe a karo na biyu a shekara ta 2007 ya kuma kammala a shekarar 2011.
A halin yanzu ɗan jam'iyar All Progressives Congress (APC) kuma sanata mai ci daga Jihar Gombe.
Mohammed Danjuma Goje | |||||||||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|
13 ga Yuni, 2023 - District: Gombe Central
13 ga Yuni, 2023 - District: Gombe Central
11 ga Yuni, 2019 - 11 ga Yuni, 2023 District: Gombe Central
ga Yuni, 2015 - 9 ga Yuni, 2019 District: Gombe Central
Mayu 2011 - Mayu 2015 District: Gombe Central
29 Mayu 2003 - Mayu 2011 ← Abubakar Habu Hashidu - Ibrahim Hassan Dankwambo → District: Gombe Central | |||||||||||||
Rayuwa | |||||||||||||
Cikakken suna | Mohammed Danjuma Goje | ||||||||||||
Haihuwa | Acre (en) , 10 Oktoba 1952 (71 shekaru) | ||||||||||||
ƙasa | Najeriya | ||||||||||||
Ƙabila | Hausawa | ||||||||||||
Harshen uwa | Hausa | ||||||||||||
Karatu | |||||||||||||
Makaranta | Jami'ar Ahmadu Bello | ||||||||||||
Harsuna | Turanci Hausa Fillanci | ||||||||||||
Sana'a | |||||||||||||
Sana'a | ɗan siyasa | ||||||||||||
Imani | |||||||||||||
Addini | Musulunci | ||||||||||||
Jam'iyar siyasa | All Progressives Congress |
A zaɓen watan Afrilun Shekarar 2011, Mohammed Danjuma Goje ya nemi takarar zama sanata mai wakiltar Gombe ta tsakiya karkashin tikitin jam'iyar PDP. Ya karanta kimiyyar Siyasa a Jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya taba zama dan majalisar Jihar Bauchi daga shekarar 1979 zuwa shekarar 1983. Goje ya rike Sakatare a National Institute For Medical Research dake Yaba Jihar Lagos, a shekara ta 1984-1989. Ya kafa ta shi kamfanin mai suna, Zaina Nigeria Ltd, a shekarar alif ta 1989 zuwa shekara ta 1999. Ya zama kamfanin suna ne daga sunan Mahaifiyarsa, Hajiya Zainab. Danjuma Goje ya nemi takarar kujerar sanata a Nigerian National Assembly a shekarar 1998 daga nan ya zama Minister of State, Power and Steel daga shekarar 1999-2001 karkashin Shugaban cin Olusegun Obasanjo..
An haifi Goje a Pindiga, a karamar hukumar Akko, jihar Gombe.
.
This article uses material from the Wikipedia Hausa / هَوُسَ article Mohammed Danjuma Goje, which is released under the Creative Commons Attribution-ShareAlike 3.0 license ("CC BY-SA 3.0"); additional terms may apply (view authors). An samar da dukkan muƙaloli a ƙarƙashin lasisin Creative Commons Attribution/Share-Alike; tana yiwuwa wasu ƙa'idoji su yi tasiri. Ku duba Ka'idojin Amfani na Gidauniyar Wiki domin ƙarin bayani. Images, videos and audio are available under their respective licenses.
®Wikipedia is a registered trademark of the Wiki Foundation, Inc. Wiki Hausa / هَوُسَ (DUHOCTRUNGQUOC.VN) is an independent company and has no affiliation with Wiki Foundation.