Jihar Kaduna wace Ake mata kirari da (Cibiyar Ilimi), ta samu wannan sunan ne a Allah ya azurta ta da makarantu na Ilimi, Kaduna jiha ce dake a Arewacin Najeriya.
Babbar cibiyar birnin Jihar na da suna Kaduna, wanda ta kasance birni ta 8 mafi girma daga cikin biranen ƙasar Najeriya. Kamar yadda yake dangane a ƙiyasin shekara ta 2006. An ƙirƙiri Jihar Kaduna shekara 7 bayan samun ƴancin kai, an ƙirƙire ta a shekarar 1967, da sunan Jihar Tsakiyar Arewa, wadda kuma ta haɗa da Jihar Katsina ta yanzu, Kaduna ta samu iyakar ta ne a shekarar 1987. Kaduna Ita ce jiha ta uku mafi girman ƙasa kuma ta haɗa da yawan mutane daga cikin sauran Jihohin Najeria, ana kuma ma Jihar Kaduna laƙabi ko kirari da Cibiyan koyon Ilimi (Centre of Learning,) saboda ta kasance tana da manyan makarantu na gaba da sakandare masu muhimmanci, kamar su Jami'ar Ahmadu Bello, Jami'ar Tsaro ta Najeriya da dai sauran su.
Kaduna | |||||
---|---|---|---|---|---|
Kaduna State (en) | |||||
| |||||
| |||||
Suna saboda | Kaduna | ||||
Wuri | |||||
| |||||
Ƴantacciyar ƙasa | Najeriya | ||||
Babban birni | Kaduna | ||||
Yawan mutane | |||||
Faɗi | 8,252,366 (2016) | ||||
• Yawan mutane | 179.19 mazaunan/km² | ||||
Harshen gwamnati | Turanci | ||||
Labarin ƙasa | |||||
Yawan fili | 46,053 km² | ||||
Sun raba iyaka da | |||||
Bayanan tarihi | |||||
Mabiyi | Jihar Arewa ta Tsakiya | ||||
Ƙirƙira | 1976 | ||||
Tsarin Siyasa | |||||
Majalisar zartarwa | Majalisar zartaswa ta jihar Kaduna | ||||
Gangar majalisa | Kaduna State House of Assembly (en) | ||||
Bayanan Tuntuɓa | |||||
Lambar aika saƙo | 720001 | ||||
Kasancewa a yanki na lokaci | |||||
Lamba ta ISO 3166-2 | NG-KD | ||||
Wasu abun | |||||
| |||||
Yanar gizo | kdsg.gov.ng |
Jihar Kaduna ta samo sunan ta Kaduna ne daga kalmar kada, jam'in kalmar Kadduna, sai aka cire harafin ''D" sai ya koma "Kaduna". A wani ƙaulin kuma, an ce kalmar ta Kaduna ta samo asali ne daga yaran Gwari, sun kasance Odna suna nufin "Kogi" kasancewar kaduna a zagaye take da rafuka. Tambarin Jihar Kaduna dai shi ne hoton Kada.
A zance mafi inganci ba a san lokacin da mutane suka fara rayuwa ba a yankin Kaduna, amma akan iya tina garin a wasu ma'aunai na tarihi da suka shuɗe, kuma hakan ya faru ne kasancewar yawan ƙabilun da ke zaune a cikin garin, Haƙiƙa birnin ya kafu ne tun kafin zamanin Usman ɗan Fodiyo wato tun tale-tale can a shekarun baya, birnin Kaduna ya kasance cibiyar jamhuriyyar Arewa tun daga shekarar 1917, har zuwa shekarar 1967, tarihi ya nuna cewa an mallake kaduna ne ga masu mulkin mallaka na turawan ƙasar Birtaniya, babban kwamandan yaƙin mulkin mallaka Frederick Lugard ya kwace Kaduna a shekarar 1897, da shi da sauran yan koransa. Daga baya kuma suka yi hadin gwuiwa tsakanin Kudancin Najeriya da kuma arewacin Najeriya a shekarar 1914. Wasu daga cikin tsofaffin garuruwan Kaduna sun haɗa da Zariya, Kafanchan da kuma Nok, wanda waɗannan garuruwan tarihi ya kasa riskan farkon garuruwan da tarihinsu tun asali. Garin Zaria shi ne tsohon gari a duk faɗin yankin Kaduna, wanda ake tunanin an kafa garin ne a shekarar 1536, wanda a wannan lokacin garin baya da suna, amma daga bisani ana kiran garin da sunan wata shahararriyar sarauniya wato Amina (Sarauniya Amina).
Sannan Kaduna ta kasance cibiyar addinin musulunci a yankin arewa, kuma daga ciki ne aka baiwa Katsina jiha. Kaduna birni ne na Hausawa ko dayake daga baya Kaduna ta kasance tana ɗaya daga cikin manyan biranen da sukafi tara kabilu daban-daban, a kalla akwai kabilu a cikin Kaduna da suka kusan 57. Jihar Kaduna a da ta hada manyan jahohi a cikinta irin su Katsina, kafin daga bisani aka cire su aka mayar da su Jihohi masu zaman kansu, a da Jihar Kaduna ita ce babban birnin tarayyar yankin arewacin najeriya a zamanin mulkin mallaka na turawa, kafin a bata babban birnin, da Zungeru a1903 zuwa1923) dake Lokoja a (1897 zuwa 1903) su ne manyan biranan. A shekarar 1923 zuwa 1966 aka bama Kaduna babban birnin tarayyar yankin arewacin najeriya. Jahar Kaduna ita ce ta huɗu 4 a jadawalin jihohin da suka fi fadin kasa a Najeriya, kuma sannan ita ce ta 3 a jihohin da suka fi kowane yawan mutane a Najeriya. Babban birnin Jihar Kaduna Shi ne Kaduna
Jihar Kaduna tana da matuƙar faɗin gaske, wanda faɗin ƙasar ta ya kai kimanin kilomita 46,053 km2, Kaduna ita ce jiha ta Huɗu da ta fi kowacce jiha girman ƙasa, kuma tana da ƙananan hukumomi guda 23, kowacce ƙaramar hukuma ta na da shugaba da ƙananan garuruwa, ƙananan hukomomi su ne kamar haka:
Adadi | Karamar Hukama | Fadin Kasa | Shuwagabanni |
---|---|---|---|
1 | Birnin Gwari | ||
2 | Chikun | ||
3 | hukumar Giwa | ||
4 | Igabi | ||
5 | Ikara | ||
6 | Jaba | ||
7 | Jama'a | ||
8 | Kachia | ||
9 | Kaduna ta arewa | ||
10 | Kaduna ta kudu | ||
11 | Kagarko | ||
12 | Kajuru | ||
13 | Kaura | ||
14 | Kauru | ||
15 | Kubau | ||
16 | Kudan | ||
17 | Lere | ||
18 | Makarfi | ||
19 | Sabon-Gari | ||
20 | Sanga | ||
21 | Soba | ||
22 | Zangon-Kataf | ||
23 | Zariya |
A jihar Kaduna, akwai masu mulki daban-daban da suka haɗa da sarakuna, zaɓaɓɓun shuwagabanni na mulkin dimukuradiya, a jihar ta Kaduna akwai Gwamna, Ƴan Majalisa, ƴan majalisar Dattijai, da kuma Sarakuna masu mulkin gargajiya. Shuwagabanni a ɓangaren dimukuradiya ana zaɓen su ne duk bayan shekaru Huɗu, su kuma sarakunan gargajiya suna gada ne a wajen iyaye da kakanni, kuma zasu iya yin mulki iya tsawon rayuwar su, amma gwamna yana da cikakken ikon da zai iya cire/nada kowane sarki a jihar sa.
A jihar Kaduna, akwai gwamna da mataimakin gwamna, kuma wadannan su ne masu cikakken mulki a cikin jihar ta Kaduna, kuma zaben su ake yi a duk bayan shekaru hudu, wanda yanzu haka Mallam Uba sani shi ne gwamnan jihar Kaduna da kuma Hadiza Sabuwa Balarabe a matsayin mataimakiyar gwamnan jihar ta Kaduna. A tsarin mulkin dimokuraɗiyya akwai ƴan majalisun jiha masu kula da dokokin jihar da kuma tsarinta, sannan akwai sanatoci uku masu kula da yanki uku na Jihar Kaduna su ne; Suleiman Abdu Kwari, Danjuma Laah da kuma Uba Sani.
Akwai sarakuna da hakimai a kowanne karamar hukuma da kuma gunduma, amman da manyan sarakunan gargajiya su ne kamar haka; Sarkin Zazzau Shehu Idris, sarkin Birnin gwari, sarkin Nok da kuma sarkin Kafanchan, wadannan sarakunan suna da ka'idojin salan mulki ga iya mutanan su kadai, sannan gwamnan jahar yana da cikakken ikon da zai sauke su ya daura wanda yake so.
Jahar Kaduna jaha ce mai tarin al’adu da ire-iren abinci daban-daban Kamar haka:
Tuwon masara da na dawa,da na gero da ɗan wake da dambu da fate da doya da dankalin Hausa da rogo da koko da dai sauran su.
Addinai biyu sune manyan addinan jahar Kaduna, wato addinin Musulunci da kuma addinin kiristanci, kasancewar addinai ne manya akwai alaka mai tsami a tsakaninsu musamman a shekara ta 2000 zuwa ta 2001 an samu rikicin addini a jahar kaduna a bisa dalilin sharia'ar Musulunci da musulmai sukai kokarin assasawa amma sai aka samu rashin jituwa da kiristoci wai suna tsammanin in har shari'ar musulunci ta kafu, to suma zai shafesu shi yasa suka ki amincewa a dalilin haka rikici ya balle inda aka samu asarar rayuka da dimbin dukiya mai tarin yawa, bayan haka akasa Mutane 1000 suka rasa rayukansu. Bayan haka an kara samun rikicin addini a shekarar 2002 amma a halin yanzu akwai zamantakewa mai karfi tsakanin addinan guda biyu.
File: sultan bello mosque by Anasskoko 03.jpg\masallacin da yamma
A fagen Ilmi kaduna ce cibiyar ilimi a arewacin Najeriya kaduna ce cibiyar makarantar horar da jami'an tsaro ta kasa wato Nigeria Defence Academy an kafaTa ne tun a shekarar 1964. Sai kuma babbar makarantar kimiyya da fasaha dake kaduna, wato Kaduna Polytechnic an kafa ta ne a shekarar 1968, sai kuma jami'ar Ahmadu Bello dake Zariya ita kuma ta kafu a shekarar 1962.Bayan haka akwai Jami'ar jahar Kaduna (kasu) da Nuhu bamalli polytechnic Zaria da college of education gidan waya da dai sauran manyan cibiyoyin ilimi. Lallai kaduna duniya ce ta ilmi wannan dalilin ne yasa kaduna tayi fice a jahohin Nigeria ta ko'ina ana barkowa daga sassa daban-daban na Najeriya ana wajajeu n neman ilimi a jahar ta kaduna domin ita jahar kaduna ta bambanta da sauran jahohin Arewacin Najeriya.
A cikin jahar kaduna ana karantar da ilimin addini matuka, cibiyar addini na bangaren Izala, shi'a, Ɗariƙar Tijjaniya da salafiyya duka suna cikin garin jahar kaduna
Akwai dandalin Murtala Mohammed Square inda ake wasanni da kuma motsa jiki, a ciki akwai Kaduna Polo Club da kuma Kaduna Golf Club kuma akwai sitadiyam mai suna Ahmadu Bello Stadiyam da Ranchers Bees Stadiyam
A.M masu nisan zango sun hada da:
F.M masu matsakaicin zango sun hada da:
Kaduna cibiya ce ta masana'antun arewa, kamar masana'antar karafa, masaka,matatar man fetur ta ƙasa, ginin tukwane, Kaduna garine wanda ake kasuwanci kasancewar yawan mutane da kuma cunkosa, akwai kasuwanni dayawa a cikin garin kaduna,galibi ma kusan kowanne anguwa a cikin babban birnin kaduna tana da kasuwan ta.
A cikin kaduna akwai babban kampanin matatan mai, me suna kaduna Refining and Petrochemical Company (KRPC),wanda daya ne daga cikin manyan kampanonin matatan mai da'ake dasu a Najeriya
Jahar tana da manyan kasuwanni kaman su kusuwan kasuwar sheikh Abubakar gumi,fanteka,kasuwar chechenia, kasuwan magani,kasuwar kawo, kasuwar bacci,kasuwan tudun wadan zaria.
Babbar hanyar data ratsa ta cikin gari ana kiranta Ahmadu Bello way. Kaduna tanada babbar kasuwa wadda aka gina tun a shekarun 1990s bayan ta fuskanci mahaukaciyar gobara. Acikin garin kaduna akwai hanyoyin jiragen kasa wadda ake sufuri daga kaduna zuwa wasu sassan Najeriya.
Akwai hanyoyin layin dogo na jiragen kasa wadanda aka gina tun a watan satumba shekarar alif 2009 mai nisan tazarar kilomita 1,435 mm (4ft 81/2) zuwa babban birnin tarayya Abuja.
bayan haka akwai filayen jiragen sama guda biyu wato Filin Jirgin Saman Jihar kaduna da kuma filin jirgin sama na chanchangi wato Chanchangi Airlines wadda ake sufuri daga jahar zuwa jaha ko daga Nigeria zuwa kasashen ketare.
Jahar kaduna tana da hukumar dake kula da tafiye-tafiye a fannoni sifirin motoci, wacce ak kira da KSTA.
.
Jihohin Najeriya |
Babban birnin tarayyar (Abuja) | Abiya | Adamawa | Akwa Ibom | Anambra | Bauchi | Bayelsa | Benue | Borno | Cross River | Delta | Ebonyi | Edo | Ekiti | Enugu | Gombe | Imo | Jigawa Kaduna | Kano | Katsina | Kebbi | Kogi | Kwara | Lagos | Nasarawa | Neja | Ogun | Ondo | Osun | Oyo | Plateau | Rivers | Sokoto | Taraba | Yobe | Zamfara |
This article uses material from the Wikipedia Hausa / هَوُسَ article Kaduna (jiha), which is released under the Creative Commons Attribution-ShareAlike 3.0 license ("CC BY-SA 3.0"); additional terms may apply (view authors). An samar da dukkan muƙaloli a ƙarƙashin lasisin Creative Commons Attribution/Share-Alike; tana yiwuwa wasu ƙa'idoji su yi tasiri. Ku duba Ka'idojin Amfani na Gidauniyar Wiki domin ƙarin bayani. Images, videos and audio are available under their respective licenses.
®Wikipedia is a registered trademark of the Wiki Foundation, Inc. Wiki Hausa / هَوُسَ (DUHOCTRUNGQUOC.VN) is an independent company and has no affiliation with Wiki Foundation.