Ibrahim Ahmad Maqari an haifeshi a ranar 15 ga watan Satumba, shekarar 1976, a birnin Zariya, da ke jihar Kaduna, Najeriya.
Farfesa Maqari malamin Addinin Musulunci ne a Najeriya dama wajen Najeriya kuma masanin lugah (larabci) yana kuma tafsirin Alqur'ani mai girma a watan Ramadan kuma limamin Masallacin ƙasa na Abuja a Najeriya.
Ibrahim Ahmad Maqari | |
---|---|
Rayuwa | |
Haihuwa | 15 Satumba 1976 (47 shekaru) |
Sana'a |
An haifi Farfesa Ibrahim Maqari a Zariya, mahaifinsa ma'aikacin gwamnati ne kuma malami. Kakansa dan asalin jihar Borno ne yazo garin Zariya ne don neman Ilimi bayan ya sami abinda ya samu na ilimin addinin Musulunci da Fiqh, sai ya yanke shawarar komawa gida don ci gaba da koyarwa a garinsu Borno, sai dai Sarkin Zazzau na wancan ƙarnin yaƙi yarda ya bar garin Zariya, har Sarkin yake cewa "Malamai basa zuwa garin shi su bar garin" sai sarki ya ba shi gida ya zauna a kusa da Masarautar Zazzau.
Farfesa Ibrahim Maqari ya fara karatun firamare ne a Jihar Katsina a shekarar 1987. Sheikh Ibrahim Maqari ya haddace Alqur'ani mai girma yana ɗan shekara 13-14 a Madarasatul Faidatul Islamiyya ta gidan Sheikh Yahuza Zariya. Daga nan sai ya tafi Kwalejin Nazarin Larabci ta Jama’atu da ke Zariya, Kaduna don yin karatun sakandire. Ya yi karatun digiri na farko a Jami'ar Al-Azhar da ke birnin Alkahira a shekarar 1999. Ya kuma yi digiri na biyu a Jami'ar Ahmadu Bello a shekarar 2005. Daga nan kuma ya tafi Jami'ar Bayero Kano don samun digirin digirgir a shekarar 2009, inda ya samu digiri na biyu a cikin shekaru biyu. A shekarar 1999, ya fara koyarwa a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya. Ya zama babban malami a Jami'ar Jihar Kaduna a shekarar 2010. Bayan ya shafe kusan shekara ɗaya yana koyarwa, Farfesa Ibrahim Maqari ya koma Jami’ar Bayero Kano inda yayi karatun Farfesanci a sashen Larabci da Harsuna, inda ya yi ritaya da kansa a shekarar 2020. Malam ya yi karatu gwargwado a gidan shahararren malami a garin Katsina Sheikh Abba Abu. Sheikh Ibrahim Maqari ya ɗauki karatu daga malamai da dama a cikin garin Zariya, a cikinsu akwai malam Tanimu Kusfa, shahararren malamin fiqihu da sauran fannonin ilimi. Sannan akwai Malam Bala Kusfa wanda ƙanin Mahaifinsa yake ɗaukan sa suna zuwa tare. Sheikh Ibrahim Ahmad Maqari yayi karatu a ƙasar Masar inda a Chan ne ya haɗu da Sheik Muhammadu Amin Abdullahi mutumin Okene.
Malam Ibrahim Maqari ya rubuta littafai da dama wanda adadinsu ya kai kusan 40 ga kaɗan daga cikin su:
Farfesa Ibrahim Ahmad Maqari Shine Limamin Masallacin Ƙasa da ƙasa dake Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
This article uses material from the Wikipedia Hausa / هَوُسَ article Ibrahim Ahmad Maqari, which is released under the Creative Commons Attribution-ShareAlike 3.0 license ("CC BY-SA 3.0"); additional terms may apply (view authors). An samar da dukkan muƙaloli a ƙarƙashin lasisin Creative Commons Attribution/Share-Alike; tana yiwuwa wasu ƙa'idoji su yi tasiri. Ku duba Ka'idojin Amfani na Gidauniyar Wiki domin ƙarin bayani. Images, videos and audio are available under their respective licenses.
®Wikipedia is a registered trademark of the Wiki Foundation, Inc. Wiki Hausa / هَوُسَ (DUHOCTRUNGQUOC.VN) is an independent company and has no affiliation with Wiki Foundation.